A cewar Kamfanin Dillancin Labaran Hauza, a cikin sanarwar Majalisar Tsaron Ƙasa ta Iran game da amincewar Amurka da sharudan Iran an bayyana cewa: Iran ta samu babbar nasara kuma ta tilasta wa Amurka ta amince da sharuda 10 na Iran. A cikin wannan shiri, Amurka ta amince da ka’idoji kamar: ba za ta kai hari ga Iran ba, Iran ta ci gaba da kula da mashigin Hormuz, amincewa da shirin tace uranium (ingantawa), dage dukkan takunkumin farko da na biyu, kawo karshen dukkan kudurorin Kwamitin Tsaro na Majalisar Dinkin Duniya da Hukumar Kula da Makaman Nukiliya (IAEA), biyan diyya ga Iran, fitar da sojojin Amurka daga yankin, da kuma dakatar da yaki a dukkan bangarori ciki har da yaki da kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Lebanon.
Ga cikakken bayanin sanarwar:
Da sunan Allah Mai Rahama Mai Jin Kai
Ana sanar da al’ummar Iran masu daraja, masu girma da jarumta cewa:
Abokan gaba a yakin da suka kaddamar cikin rashin adalci, sabawa doka da kuma ta’addanci a kan al’ummar Iran sun fuskanci mummunar shan kashi na tarihi wanda ba za a iya musantawa ba. Da albarkacin jinin shahidan juyin juya halin Musulunci, Jagora mai girma na juyin juya hali, da kuma jarumtar mayaƙan Iran a filayen yaki – musamman ma halartar al’umma tun daga farkon yakin – Iran ta samu babbar nasara kuma ta tilasta wa Amurka ta amince da shiaruda 10 nata.
A cikin wannan shiri Amurka ta amince da muhimman ka’idoji kamar: tabbatar da rashin kai hari ga Iran, ci gaba da ikon Iran a mashigin Hormuz, amincewa da tace uranium, dage dukkan takunkumi, kawo karshen dukkan kudurorin hukuma na Majalisar Dinkin Duniya da IAEA, biyan diyya ga Iran, fitar da sojojin Amurka daga yankin, da kuma dakatar da yaki a dukkan gaban yaki ciki har da Lebanon.
Majalisar ta taya al’ummar Iran murna kan wannan nasara mai girma, tare da jaddada cewa har yanzu akwai bukatar juriya, hikima daga jami’an gwamnati, da kuma kiyaye hadin kan al’umma har sai an kammala cikakkun bayanan wannan nasara.
A cikin kwanaki 40 da suka gabata, Iran da abokan gwagwarmayarta a Lebanon, Iraki, Yemen da Falasdinu sun kai munanan hare-hare ga abokan gaba wanda tarihin duniya ba zai manta da su ba. Iran da kawancen gwagwarmaya sun lalata manyan kayayyakin soja, tushe da manyan kadarorin makiya a yankin, tare da tilasta musu fahimtar cewa ba su da ikon cin nasara a wannan yaki.
Tun kusan kwanaki goma bayan fara yakin, makiya sun fahimci cewa ba za su iya samun nasara ba, don haka suka fara neman hanyoyin tuntubar Iran domin neman tsagaita wuta. Duk da haka, Iran ta ki amincewa da wadannan bukatu har sai an cimma dukkan manufofin da aka tsara.
Yanzu ana sanar da al’ummar Iran cewa kusan dukkan manufofin yakin sun cika, kuma makiya sun shiga cikin wani yanayi na rauni da shan kashi na tarihi. Don haka an yanke shawarar cewa za a fara tattaunawa a birnin Islamabad domin kammala cikakkun bayanai na wannan nasara.
Iran ta gabatar da sharuda 10 ga Amurka ta hannun Pakistan, wanda ya hada da: kula da zirga‑zirgar jiragen ruwa a mashigar Hormuz karkashin kulawar sojojin Iran, kawo karshen dukkan hare-hare kan kawancen gwagwarmaya, fitar da sojojin Amurka daga dukkan sansanoninsu a yankin, biyan dukkan diyya ga Iran, dage takunkumi, sako dukkan kadarorin Iran da aka toshe a kasashen waje, da kuma tabbatar da wannan yarjejeniya ta hanyar kuduri mai karfi na Kwamitin Tsaro na Majalisar Dinkin Duniya.
Firaministan Pakistan ya sanar da Iran cewa Amurka ta amince da wadannan ka’idoji a matsayin tushen tattaunawa. Saboda haka Iran ta amince da yin tattaunawa na makonni biyu a Islamabad domin kammala cikakkun bayanai.
An jaddada cewa wannan ba yana nufin karshen yaki ba ne. Iran za ta amince da karshen yakin ne kawai idan an kammala dukkan sharuddan da ke cikin shirin maki 10.
Za a fara tattaunawar daga ranar Juma’a 21 ga watan Farvardin (10 ga Afrilu, 2026) a Islamabad. A wannan lokacin ana bukatar al’ummar Iran su ci gaba da kiyaye hadin kai, su goyi bayan tsarin tattaunawar kasa, kuma su guji duk wata magana da za ta iya haifar da rarrabuwar kai.
Idan makiya sun cika sharuddan da aka shimfida, al’ummar Iran za su yi bikin wannan babbar nasara ta tarihi. Idan kuwa ba haka ba, Iran za ta ci gaba da yaki tare da cikakken shiri don mayar da martani ga duk wata kuskure daga bangaren makiya.
Majalisar Tsaron Ƙasar Iran
19 ga Farvardin 1405 (08 ga Afrilu, 2026)
Ra'ayinka